Wani matashi ɗan ƙasar Masar ya lashe gasar musabaƙar Al-Ƙur’ani mai girma ta duniya da aka yi a Tanzania.
Omar Mohammad Hussein, Ya samu nasarar zama zakara tsakanin abokan karawarsa 23 daga ƙasashe 23 na ciki da wajen nahiyar Afirka.
Omar ya lashe miliyan 23 na kudin Tanzania daidai da dalar Amurka dubu 10, kwatankwacin naira miliyan bakwai da ɗari hudu a kuɗin Najeriya.