fidelitybank

Ɗan majalisar Amurka ya janyo wa kansa jagwal bisa alaƙa da ɗan Najeriya

Date:

Wani dan majalisar dokokin Amurka na jam’iyyar Republican na fuskantar hadarin korarsa daga majalisar, saboda karya da ya yi kan wani tallafin kudi na siyasa da ke da alaka da wani attajiri dan Najeriya.

Masu taimaka wa alkali yanke hukunci, na tarayya sun gano cewa Jeff Fortenberry, dan majalisar wakilai daga Nebraska, ya yi wa jami’an hukumar binciken manyan laifuka ta Amurka, FBI, karya kan karbar tallafin da ya saba wa doka, daga attajiri Gilbert Chagoury, wani hamshakin attajirin dan kasuwa dan Najeriya.

Yanzu dai a sakamakon wannan bincike da masu taimaka wa alkalin suka yi inda suka gano cewa dan majalisa Jeff Fortenberry ya shirga wa jami’an na FBI, masu binciken laifuka karya game da kudin tallafin na siyasa da attajirin dan Najeriya ya ba shi, zai iya rasa kujerarsa ta wakilci a majalisar.

Sannan kuma bayan rasa kujerar, zai iya fuskantar daurin shekara 15 a gidan maza, a bisa laifuka uku.

A bisa dokar Amurka, haramun ne ga ‘yan kasashen waje su bayar da wani tallafi na siyasa, to amma kuma Mista Chagoury, mai shekara 75, ya dade yana yin hakan.

A shekara ta 2019, gwamnatin Amurka ta ci tararsa dala miliyan 1.8, kuma aka gudanar da bincike a kan wasu daga cikin wadanda suka ci moriyar tallafin nasa.

A shekara ta 2016, ne ya bayar da tallafin da ya saba doka na dala dubu 30 ga dan majalisa Fortenberry, amma ta hannun wasu masu bayar da tallafi a yayin wani taro a Los Angeles

Ana sa ran yanke masa hukunci a ranar 28 ga watan Yuni, amma kuma ya ce zai dukaka kara. A cewar BBC.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp