fidelitybank

Ɗan majalisar Amurka ya janyo wa kansa jagwal bisa alaƙa da ɗan Najeriya

Date:

Wani dan majalisar dokokin Amurka na jam’iyyar Republican na fuskantar hadarin korarsa daga majalisar, saboda karya da ya yi kan wani tallafin kudi na siyasa da ke da alaka da wani attajiri dan Najeriya.

Masu taimaka wa alkali yanke hukunci, na tarayya sun gano cewa Jeff Fortenberry, dan majalisar wakilai daga Nebraska, ya yi wa jami’an hukumar binciken manyan laifuka ta Amurka, FBI, karya kan karbar tallafin da ya saba wa doka, daga attajiri Gilbert Chagoury, wani hamshakin attajirin dan kasuwa dan Najeriya.

Yanzu dai a sakamakon wannan bincike da masu taimaka wa alkalin suka yi inda suka gano cewa dan majalisa Jeff Fortenberry ya shirga wa jami’an na FBI, masu binciken laifuka karya game da kudin tallafin na siyasa da attajirin dan Najeriya ya ba shi, zai iya rasa kujerarsa ta wakilci a majalisar.

Sannan kuma bayan rasa kujerar, zai iya fuskantar daurin shekara 15 a gidan maza, a bisa laifuka uku.

A bisa dokar Amurka, haramun ne ga ‘yan kasashen waje su bayar da wani tallafi na siyasa, to amma kuma Mista Chagoury, mai shekara 75, ya dade yana yin hakan.

A shekara ta 2019, gwamnatin Amurka ta ci tararsa dala miliyan 1.8, kuma aka gudanar da bincike a kan wasu daga cikin wadanda suka ci moriyar tallafin nasa.

A shekara ta 2016, ne ya bayar da tallafin da ya saba doka na dala dubu 30 ga dan majalisa Fortenberry, amma ta hannun wasu masu bayar da tallafi a yayin wani taro a Los Angeles

Ana sa ran yanke masa hukunci a ranar 28 ga watan Yuni, amma kuma ya ce zai dukaka kara. A cewar BBC.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp