fidelitybank

Ɗan bayan Faransa Disasi ya koma Chelsea

Date:

Dan wasan baya na kasar Faransa,Axel Disasi, ya koma Chelsea daga Monaco kan kwantiragin shekara shida akan Yuro miliyan 45 (£38.57m).

Disasi, mai shekaru 25, ya koma kungiyar ta Stamford Bridge bayan Wesley Fofana ya samu mummunan rauni a gwiwa.

Ya buga dukkan wasanni 38 a gasar Ligue 1 ta Monaco a kakar wasan da ta wuce.

Disasi ya buga wa Faransa wasa sau hudu, ciki har da wanda ya shigo daga baya a wasan ƙarshe na cin Kofin Duniya na 2022 da Faransa ta fafata da Argentina, kuma ya buga wa Monaco wasanni 129 bayan ya koma daga Stade de Reims a watan Agustan 2020.

Dan wasan ya zama na shida da Chelsea ta saya a bazara bayan sayen Christopher Nkunku da Nicolas Jackson da Lesley Ugochukwu da Angelo Gabriel da kuma Diego Moreira, yayin da sabon koci Mauricio Pochettino ke ci gaba da sanya tambarinsa a kan kungiyar.

A halin da ake ciki, Chelsea ta amince da farashi mai tsaron gida Robert Sanchez da Brighton, yayin da Brighton ta cigaba da kin amincewa da tayin da Chelsea ke yi kan dan wasan tsakiya Moises Caicedo.

Chelsea ta kammala wasannin share fage a ranar Lahadi da ta yi kunnen doki ci 1-1 da Borussia Dortmund a birnin Chicago – wanda ya kawo karshen rangadin da suka yi a Amurka ba tare da an doke ta ba.

Kuma yanzu hankali ya koma kan wasansu na farko na gasar Premier na 2023/24 a gida da Liverpool ranar 13 ga watan Agusta.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp