Aminu Mohammed dalibin shekarar karshe a jami’ar tarayya dake Dutse, ya nemi gafarar uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari kan sukar da yayi mata.
Mohammed ya bayyana a shafinsa na twitter a cikin harshen Hausa cewa Aisha ta ci kuɗin talakawa ta yi ƙiba.
Jami’an tsaro ne suka kama shi sannan suka gurfanar da shi a gaban babban kotun tarayya mai lamba 14 na babban birnin tarayya Abuja.
Sai dai Aisha a ranar Juma’a ta janye karar da ta shigar a kan Aminu Adamu Mohammed.
Lauyan da ke shigar da kara, Fidelis Ogbobe, ya ce janyewar ta biyo bayan tsoma bakin wasu ‘yan Najeriya masu kishin kasa.
Da yake rubuta a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi, Mohammed ya ce ba shi da niyyar cutar da ita.
“Zan kuma yi amfani da wannan kafar domin nuna godiya ta ga wadanda suka taimaka min na shiga cikin mafi duhun sa’o’in rayuwata, mutum ba zai iya kubuta daga kaddararsa ba, amma abin da ya faru ya kamata ya zama darasi ga dukkanmu. Na gode duka da ƙauna ɗaya.
“Zan so na yi amfani da wannan kafar domin bayyana bata haƙuri ga wadanda na cutar da su musamman mahaifiyarmu Aisha Buhari. Ba burina bane in cutar da ku kuma insha Allahu zan canza da kyau. Duk da haka, ni ma na gode da gafarar ku, na gode mama.”