fidelitybank

Ɗalibin da ya caccaki Aisha Buhari ya ba ta haƙuri

Date:

Aminu Mohammed dalibin shekarar karshe a jami’ar tarayya dake Dutse, ya nemi gafarar uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari kan sukar da yayi mata.

Mohammed ya bayyana a shafinsa na twitter a cikin harshen Hausa cewa Aisha ta ci kuɗin talakawa ta yi ƙiba.

Jami’an tsaro ne suka kama shi sannan suka gurfanar da shi a gaban babban kotun tarayya mai lamba 14 na babban birnin tarayya Abuja.

Sai dai Aisha a ranar Juma’a ta janye karar da ta shigar a kan Aminu Adamu Mohammed.

Lauyan da ke shigar da kara, Fidelis Ogbobe, ya ce janyewar ta biyo bayan tsoma bakin wasu ‘yan Najeriya masu kishin kasa.

Da yake rubuta a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi, Mohammed ya ce ba shi da niyyar cutar da ita.

“Zan kuma yi amfani da wannan kafar domin nuna godiya ta ga wadanda suka taimaka min na shiga cikin mafi duhun sa’o’in rayuwata, mutum ba zai iya kubuta daga kaddararsa ba, amma abin da ya faru ya kamata ya zama darasi ga dukkanmu. Na gode duka da ƙauna ɗaya.

“Zan so na yi amfani da wannan kafar domin bayyana bata haƙuri ga wadanda na cutar da su musamman mahaifiyarmu Aisha Buhari. Ba burina bane in cutar da ku kuma insha Allahu zan canza da kyau. Duk da haka, ni ma na gode da gafarar ku, na gode mama.”

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp