fidelitybank

Ɗalibin da ya caccaki Aisha Buhari ya ba ta haƙuri

Date:

Aminu Mohammed dalibin shekarar karshe a jami’ar tarayya dake Dutse, ya nemi gafarar uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari kan sukar da yayi mata.

Mohammed ya bayyana a shafinsa na twitter a cikin harshen Hausa cewa Aisha ta ci kuɗin talakawa ta yi ƙiba.

Jami’an tsaro ne suka kama shi sannan suka gurfanar da shi a gaban babban kotun tarayya mai lamba 14 na babban birnin tarayya Abuja.

Sai dai Aisha a ranar Juma’a ta janye karar da ta shigar a kan Aminu Adamu Mohammed.

Lauyan da ke shigar da kara, Fidelis Ogbobe, ya ce janyewar ta biyo bayan tsoma bakin wasu ‘yan Najeriya masu kishin kasa.

Da yake rubuta a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi, Mohammed ya ce ba shi da niyyar cutar da ita.

“Zan kuma yi amfani da wannan kafar domin nuna godiya ta ga wadanda suka taimaka min na shiga cikin mafi duhun sa’o’in rayuwata, mutum ba zai iya kubuta daga kaddararsa ba, amma abin da ya faru ya kamata ya zama darasi ga dukkanmu. Na gode duka da ƙauna ɗaya.

“Zan so na yi amfani da wannan kafar domin bayyana bata haƙuri ga wadanda na cutar da su musamman mahaifiyarmu Aisha Buhari. Ba burina bane in cutar da ku kuma insha Allahu zan canza da kyau. Duk da haka, ni ma na gode da gafarar ku, na gode mama.”

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp