fidelitybank

Ɗalibin da a kai garkuwa da shi ya ƙi dawowa gida, ya ce ya fi jin daɗin zama da ƴan ta’addan

Date:

 

 

 

Ɗalibi ɗaya tilo da ya yi saura a hannun ƴan fashin dajin da su ka yi garkuwa da ɗalibai 121 na Makarantar Bethel Baptist High School a Jihar Kaduna ya ce ya fi jin daɗin zama a hannun ƴan ta’addan.

A tuna cewa a ranar 5 ga watan Yulin 2021 ne ƴan ta’addan su ka kutsa kai cikin makarantar da ke kan titin Kaduna-Kachia, a ƙauyen Damishi, da ke Ƙaramar Hukumar Chikun su ka yi awon-gaba da ɗaliban.

Jaridar Vanguard ta rawaito cewa Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Ƙasa, CAN, reshen Jihar Kaduna, Rabaran Joseph John Hayab ne ya baiyana hakan.

A cewar sa “ɗalibi ɗaya da ya yi saura a hannun ƴan fashin daji, wanda shi ne mafi kankanta a cikin su, ya ce ba zai dawo gida ba.

“Ya ce shi zai ci gaba da zama da ƴan fashin dajin. Wannan abin al’ajabi ne ga ɗaukacin ƴan ɗariƙar Baptist da ma CAN baki ɗaya.

“An ce wai ƴan ta’addan na bashi kyautar kayaiyaki ne duk sanda su ka je su ka kai hari su ka dawo, shi ya sa ya ki yadda ya dawo gida.

“Ina ganin wayo su ka yi wa yaron su ka riƙa bashi kayan daɗi domin su yaudari zuciyarsa ya ji baya son komawa gida. An ce wai yaron ya ma gaya musu cewa shi ba ya son komawa wajen iyayen sa saboda wai dama dukan sa a ke yi gida idan yai laifi.

Hayab ya ƙara da cewa shima mutumin da ya saba kai wa ƴan ta’addan kuɗin fansa sun riƙe shi bayan da ya ke kai kuɗin fansar shi wannan yaron da ya ce ba zai dawo ba.

“Gaba ɗaya ma lamarin ya jefa mu cikin ruɗani. Shi mutumin da ya saba kai musu kuɗaɗen fansa, ko me ya faru?, ya je kai kuɗin fansar shi wannan yaron, ƴan ta’addan sun riƙe shi.

“To gaba ɗaya lamarin ya ɗauki wani sako na daban. Mu na dai roƙon Ubangiji ya kawo mana ɗauki,” in ji Hayab.

Ya kuma yi kira ga mahukunta da su dage su ƙwato yaron nan da ga hannun ƴan ta’adda da ma sauran mutanen da a ka yi garkuwa da su.

 

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp