fidelitybank

Ɗalibin da a kai garkuwa da shi ya ƙi dawowa gida, ya ce ya fi jin daɗin zama da ƴan ta’addan

Date:

 

 

 

Ɗalibi ɗaya tilo da ya yi saura a hannun ƴan fashin dajin da su ka yi garkuwa da ɗalibai 121 na Makarantar Bethel Baptist High School a Jihar Kaduna ya ce ya fi jin daɗin zama a hannun ƴan ta’addan.

A tuna cewa a ranar 5 ga watan Yulin 2021 ne ƴan ta’addan su ka kutsa kai cikin makarantar da ke kan titin Kaduna-Kachia, a ƙauyen Damishi, da ke Ƙaramar Hukumar Chikun su ka yi awon-gaba da ɗaliban.

Jaridar Vanguard ta rawaito cewa Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Ƙasa, CAN, reshen Jihar Kaduna, Rabaran Joseph John Hayab ne ya baiyana hakan.

A cewar sa “ɗalibi ɗaya da ya yi saura a hannun ƴan fashin daji, wanda shi ne mafi kankanta a cikin su, ya ce ba zai dawo gida ba.

“Ya ce shi zai ci gaba da zama da ƴan fashin dajin. Wannan abin al’ajabi ne ga ɗaukacin ƴan ɗariƙar Baptist da ma CAN baki ɗaya.

“An ce wai ƴan ta’addan na bashi kyautar kayaiyaki ne duk sanda su ka je su ka kai hari su ka dawo, shi ya sa ya ki yadda ya dawo gida.

“Ina ganin wayo su ka yi wa yaron su ka riƙa bashi kayan daɗi domin su yaudari zuciyarsa ya ji baya son komawa gida. An ce wai yaron ya ma gaya musu cewa shi ba ya son komawa wajen iyayen sa saboda wai dama dukan sa a ke yi gida idan yai laifi.

Hayab ya ƙara da cewa shima mutumin da ya saba kai wa ƴan ta’addan kuɗin fansa sun riƙe shi bayan da ya ke kai kuɗin fansar shi wannan yaron da ya ce ba zai dawo ba.

“Gaba ɗaya ma lamarin ya jefa mu cikin ruɗani. Shi mutumin da ya saba kai musu kuɗaɗen fansa, ko me ya faru?, ya je kai kuɗin fansar shi wannan yaron, ƴan ta’addan sun riƙe shi.

“To gaba ɗaya lamarin ya ɗauki wani sako na daban. Mu na dai roƙon Ubangiji ya kawo mana ɗauki,” in ji Hayab.

Ya kuma yi kira ga mahukunta da su dage su ƙwato yaron nan da ga hannun ƴan ta’adda da ma sauran mutanen da a ka yi garkuwa da su.

 

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp