fidelitybank

Ɗaliban Zamfara sun yi zanga-zanga a kan sace ɗan uwansu

Date:

Daliban Jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zanga don nuna ɓacin ransu kan sace ‘yan uwansu ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka yi a jihar.

Matafiya da dama ne suka maƙale a lokacin da fusatattun ɗaliban suka toshe babbar hanyar Gusau zuwa Funtua.

Masu zanga-zangar sun fara taruwa ne tun daga Damba zuwa Sabon-Gida da ke makwabtaka ta jami’ar.

Duk da tarin jami’an tsaron da ke birnin Gusau, ɗaliban sun toshe babbar hanyar da ke haɗa jihar da jihohin Sokoto da Katsina da kuma jihar Kaduna.

Daliban sun ce a ranar juma’a da daddare masu garkuwa da mutanen sun sace ‘yan uwansu ɗalibai a garin Damba da ke wajen birnin Gusau.

A ranar Litinin ne ake sa ran fara jarrabawa a jami’ar, to sai dai ɗaliban sun ce ba za su bari a fara jarrabawar ba, har sai an kuɓutar da ‘yan uwan nasu.

Jihar Zamfara na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da matsalar masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp