Daliban Jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zanga don nuna ɓacin ransu kan sace ‘yan uwansu ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka yi a jihar.
Matafiya da dama ne suka maƙale a lokacin da fusatattun ɗaliban suka toshe babbar hanyar Gusau zuwa Funtua.
Masu zanga-zangar sun fara taruwa ne tun daga Damba zuwa Sabon-Gida da ke makwabtaka ta jami’ar.
Duk da tarin jami’an tsaron da ke birnin Gusau, ɗaliban sun toshe babbar hanyar da ke haɗa jihar da jihohin Sokoto da Katsina da kuma jihar Kaduna.
Daliban sun ce a ranar juma’a da daddare masu garkuwa da mutanen sun sace ‘yan uwansu ɗalibai a garin Damba da ke wajen birnin Gusau.
A ranar Litinin ne ake sa ran fara jarrabawa a jami’ar, to sai dai ɗaliban sun ce ba za su bari a fara jarrabawar ba, har sai an kuɓutar da ‘yan uwan nasu.
Jihar Zamfara na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da matsalar masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa