fidelitybank

Ɗaliban Zamfara sun yi zanga-zanga a kan sace ɗan uwansu

Date:

Daliban Jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zanga don nuna ɓacin ransu kan sace ‘yan uwansu ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka yi a jihar.

Matafiya da dama ne suka maƙale a lokacin da fusatattun ɗaliban suka toshe babbar hanyar Gusau zuwa Funtua.

Masu zanga-zangar sun fara taruwa ne tun daga Damba zuwa Sabon-Gida da ke makwabtaka ta jami’ar.

Duk da tarin jami’an tsaron da ke birnin Gusau, ɗaliban sun toshe babbar hanyar da ke haɗa jihar da jihohin Sokoto da Katsina da kuma jihar Kaduna.

Daliban sun ce a ranar juma’a da daddare masu garkuwa da mutanen sun sace ‘yan uwansu ɗalibai a garin Damba da ke wajen birnin Gusau.

A ranar Litinin ne ake sa ran fara jarrabawa a jami’ar, to sai dai ɗaliban sun ce ba za su bari a fara jarrabawar ba, har sai an kuɓutar da ‘yan uwan nasu.

Jihar Zamfara na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da matsalar masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp