A ranar Litinin ne ofishin hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta ƙasa (WAEC), ya bayyana cewa, ɗaliban makarantun gwamnati na jihohin Sokoto da Zamfara ba za su za na jarrabawar watan Mayu da na Yuni da aka shirya za a fara ranar 16 ga watan Mayun 2022.
Mista Patrick Areghan, Shugaban ofishin Hukumar WAEC ta ƙasa ne ya bayyana haka, a lokacin da yake ganawa da manema labarai kan yadda ake gudanar da jarrabawar kammala sakandare ta Afirka ta Yamma (WASSCE) na shekarar 2022 ga masu neman shiga makarantu a Najeriya.
Areghan bai bayyana dalilan da suka sa aka cire su ba. An tattaro cewa dai hukumar jarabawar ta ki karbar wadanda suka fito daga Zamfara kan basussukan da ake bin su tsawon shekaru, yayin da Sokoto ba ta samu masauki ba, domin a shekarar 2021 ma’aikatar ilimi ta kasa saka wa ɗaliban ta na dole ci gaba da tantance makin (CASS).
Areghan ya bayyana cewa, makarantun gwamnati a jihohin Sokoto da Zamfara za su shiga jarrabawar watan Mayu/Yuni na 2022 ba. Ya bayyana cewa za a gudanar da jarrabawar makaranta na shekarar 2022 tsakanin 16 ga watan Mayu zuwa 23 ga watan Yunin 2022 a Najeriya, wanda zai dauki tsawon makonni shida.