fidelitybank

Ɗaliban jami’ar Tarraya a Zamfara sun shaƙi iskar ƴanci

Date:

Wasu dalibai mata biyu na Jami’ar Tarayya Gusau, da ke Jihar Zamfara, da aka yi garkuwa da su a gidan kwanan su da ke kauyen Sabon Gida a karamar Hukumar Bungudu, sun samu ‘yanci.

Kungiyar dalibai ta jihar Zamfara (ZAMSSA) reshen jami’ar tarayya ta Gusau ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na kungiyar, Kwamared Umar Abubakar.

Kungiyar ba ta bayyana ko an biya kudin fansa ko kuma a’a ba kafin daliban mata da aka yi garkuwa da su na Sashen Microbiology na Jami’ar su sami ‘yancinsu a ranar Juma’a.

Jaridar DAILY POST ta rawaito cewa, daliban mata biyu da aka yi garkuwa da su sun koma ga iyalansu bayan kwashe kwanaki 12 a hannunsu.

“Muna matukar farin ciki da samun ‘yancinmu kuma muna godiya ga mahukuntan makarantar da iyayenmu da suka shiga cikin mawuyacin hali na sace mu da zafi da damuwa mara misaltuwa”, in ji daliban.

Sanarwar ta bukaci jami’an tsaro da su tabbatar da kamawa tare da gurfanar da wadanda suka aikata laifin da kuma daukar nauyin wannan aika-aika, komai tsawon lokaci.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp