fidelitybank

Ɗalibai sun yi zanga-zanga a jami’a bayan an kashe ɗalibi

Date:

Harabar jami’ar Obafemi Awolowo, OAU, Ile-Ife, a ranar Laraba ta fuskanci zanga-zangar dalibai.

Zanga-zangar daliban ta biyo bayan kashe Okolie Arinze, wani dalibai mai digiri ajin 500 a fannin Injiniya a makarantar da yammacin ranar Litinin.

DAILY POST ta tattaro cewa daliban da suka yi zanga-zangar sun mamaye ginin kungiyar daliban, inda suka rufe shi.

Arinze, bayan an azabtar da shi bisa zargin satar wayar hannu a dakin taro na Awo dake jami’ar, an kawo gawarsa a cibiyar bada agajin gaggawa ta asibitin koyarwa na jami’ar Obafemi Awolowo dake Ile-Ife a ranar Talata.

A nata martanin hukumar jami’ar ta yi Allah wadai da lamarin.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Jami’ar Abiodun Olanrewaju ya fitar, makarantar ta bayyana cewa, mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Adebayo Simeon Bamire, ya kafa wani kwamiti domin bankado al’amuran da suka haddasa faruwar lamarin.

Sanarwar ta kara da cewa, ” Matakin da ‘yan kungiyar suka dauka, kasancewar ya saba wa dokar kasa da na jami’ar, an kai rahoto ga ‘yan sanda da suka fara bincike.”

A halin da ake ciki kuma, wata sanarwa mai dauke da sa hannun dukkan shugabannin tsangayar fasaha ta nuna cewa za a gudanar da zanga-zangar lumana don bayyana kokensu da kuma hukunta duk bangarorin da abin ya shafa.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp