fidelitybank

Ɗalibai sun yi zanga-zanga a jami’a bayan an kashe ɗalibi

Date:

Harabar jami’ar Obafemi Awolowo, OAU, Ile-Ife, a ranar Laraba ta fuskanci zanga-zangar dalibai.

Zanga-zangar daliban ta biyo bayan kashe Okolie Arinze, wani dalibai mai digiri ajin 500 a fannin Injiniya a makarantar da yammacin ranar Litinin.

DAILY POST ta tattaro cewa daliban da suka yi zanga-zangar sun mamaye ginin kungiyar daliban, inda suka rufe shi.

Arinze, bayan an azabtar da shi bisa zargin satar wayar hannu a dakin taro na Awo dake jami’ar, an kawo gawarsa a cibiyar bada agajin gaggawa ta asibitin koyarwa na jami’ar Obafemi Awolowo dake Ile-Ife a ranar Talata.

A nata martanin hukumar jami’ar ta yi Allah wadai da lamarin.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Jami’ar Abiodun Olanrewaju ya fitar, makarantar ta bayyana cewa, mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Adebayo Simeon Bamire, ya kafa wani kwamiti domin bankado al’amuran da suka haddasa faruwar lamarin.

Sanarwar ta kara da cewa, ” Matakin da ‘yan kungiyar suka dauka, kasancewar ya saba wa dokar kasa da na jami’ar, an kai rahoto ga ‘yan sanda da suka fara bincike.”

A halin da ake ciki kuma, wata sanarwa mai dauke da sa hannun dukkan shugabannin tsangayar fasaha ta nuna cewa za a gudanar da zanga-zangar lumana don bayyana kokensu da kuma hukunta duk bangarorin da abin ya shafa.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp