fidelitybank

Ɗalibai huɗu sun nutse a ruwa garin murnar cin jarabawa a Legas

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta ce, wasu matasa hudu sun nutse a ruwa a yayin da suke murnar cin jarrabawar kammala sakandire.

Lamarin ya afku ne a ranar Talata a tekun Elegushi da ke unguwar masu galihu ta Lekki.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan SP Benjamin Hundeyin, ya wallafa a shafinsa na tiwita cewa matasan sun nitse bayan sun karbi sakamakon jarrabawarsu daga makaranta.

Hukumar gudanarwar tekun ta ce mamatan na daga ckin dalibai 10 da suka je wajen don yin murnar samun nasara a jarrabawarsu ta kammala karatun sakandire.

Mai magana da yawun hukumar gudanarwar ya ce yaran sun bijirewa gargadin da jami’an da ke kula da tekun suka yi musu.

Kawo yanzu dai mahukunta ba su bayyana shekarun yaran ba ko kuma daga in da suka fito ba.

Jihar Legas dai na kewaye da ruwa da kuma wuraren shakatawa abin da ya sa mutane kanje don shakatawa ko kuma gudanar da wani biki a bakin teku.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp