fidelitybank

Ɓarawo ya rasu ya na ƙoƙarin yin sata a ƙarƙashin mota

Date:

 

 

An tsinci gawar wani mutum da a ke zargin ɓarawo ne a ƙarƙashin wata mota a Ago Egun, bodar Idiroko da ke Jihar Ogun.

Jaridar Tribune ta rawaito cewa a na zargin ɓarawon ya yi yunƙurin kwance wasu muhimman abubuwa a jikin motar, amma sai jak ɗin ɗaga mota da ya yi amfani da shi wajen ɗaga motar ya goce bayan ya riga ya shiga ƙarƙashin ta, inda motar ta faɗo masa.

Soji Gonzalo, Kwamandan rundunar bijilante ta jihar, ya baiyana cewa su na cikin sintiri ne sai su ka ga gawar mutum a ƙarƙashin wata tsohuwar mota a wani garejin gyaran mota.

Ya ƙara da cewa sun gano gawar mutumin ne da misalin ƙarfe 6 na yamma a Ago Egun ranar Alhamis.

Gonazlo ya baiyana cewa binciken su na farko ya nuna cewa motar ta daɗe a garejin wanda sama da shekara biyu ba amfani da shi kuma duk yi kurin samun wanda ya ke da filin garejin ya ci tura.

“A yanzu dai mun ɗauke gawar da kuma jak da mu ka samu mai launin ja da kuma almakashi da sauran sifanu za mu kai wa ofishin ƴan sanda na Idiroko domin faɗaɗa bincike,” in ji Gonzalo.

 

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp