fidelitybank

Ƴansandan Kano sun kuɓutar da ƴar shekara huɗu daga hannun masu garkuwa

Date:

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kuɓutar da wata ƙaramar yarinya mai shekara huɗu daga hannun masu garkuwa da mutane tare da kama wanda ake zargi da sace yarinyar.

Cikin wani saƙo jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce a ranar Talata jami’an ‘yansanda suka kama wani matashi mai suna Saifullahi Abba, mai shekara 23, bisa zargin garkuwa da yarinyar.

Tun da farko mahaifin yarinyar ne mai suna Zilkiflu Abdullahi da ke zaune a ƙauyen Dakatsalle a yankin ƙaramar hukumar Bebeji ya kai wa ‘yansanda ƙorafin sace ‘yar tasa mai suna Nabila a ranar 22 ga watan Nuwamban da muke ciki.

”Kwana guda bayan haka kuma sai wani mutum ya kira shi tare da iƙirarin sace ‘yar tasa, sannan ya buƙaci naira miliyan uku a matsayin kuɗin fansa”, kamar yadda SP Kiyawa ya bayyana.

‘Yansandan sun ce sun kama wanda suke zargi da sace yarinyar – wanda ɗan asalin ƙaramar hukumar Wudil ne – a ƙauyen Luran da ke ƙaramar hukumar Dawakin Kudu.

”Wanda ake zargin ya amince da laifin da aka tuhume shi, sannan ya jagoranci jami’an ‘yansanda zuwa inda ya ɓoye yarinyar a ƙauyen na Luran, inda nan take aka kuɓutar da ita,”Kamar yadda kakakin ‘yansandan jihar Kanon ya bayyana.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp