fidelitybank

Ƴansandan Kano sun kuɓutar da ƴar shekara huɗu daga hannun masu garkuwa

Date:

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kuɓutar da wata ƙaramar yarinya mai shekara huɗu daga hannun masu garkuwa da mutane tare da kama wanda ake zargi da sace yarinyar.

Cikin wani saƙo jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce a ranar Talata jami’an ‘yansanda suka kama wani matashi mai suna Saifullahi Abba, mai shekara 23, bisa zargin garkuwa da yarinyar.

Tun da farko mahaifin yarinyar ne mai suna Zilkiflu Abdullahi da ke zaune a ƙauyen Dakatsalle a yankin ƙaramar hukumar Bebeji ya kai wa ‘yansanda ƙorafin sace ‘yar tasa mai suna Nabila a ranar 22 ga watan Nuwamban da muke ciki.

”Kwana guda bayan haka kuma sai wani mutum ya kira shi tare da iƙirarin sace ‘yar tasa, sannan ya buƙaci naira miliyan uku a matsayin kuɗin fansa”, kamar yadda SP Kiyawa ya bayyana.

‘Yansandan sun ce sun kama wanda suke zargi da sace yarinyar – wanda ɗan asalin ƙaramar hukumar Wudil ne – a ƙauyen Luran da ke ƙaramar hukumar Dawakin Kudu.

”Wanda ake zargin ya amince da laifin da aka tuhume shi, sannan ya jagoranci jami’an ‘yansanda zuwa inda ya ɓoye yarinyar a ƙauyen na Luran, inda nan take aka kuɓutar da ita,”Kamar yadda kakakin ‘yansandan jihar Kanon ya bayyana.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp