fidelitybank

Ƴansanda sun ƙwato motar miliyan 55 da aka tsere da ita garin ɗani

Date:

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tabbatar da kwato wata mota kirar Mercedes Benz GLB 250 wadda kuɗinta yakai naira miliyan 55 da wani mai son saye ya sace.

Wani dillalin mota mai suna Mohammed Manga ya zargi Henry, wanda ya yi kama da abokin ciniki, ya tsere da motar yayin da yake gwada ta a babban birnin tarayya Abuja.

Mohammed ya ce daya daga cikin abokansa wanda kuma dillalin mota ne ya kai motar Mercedes Benz wurin wani mai son saye (Henry) domin siyar da ita, amma matsala ta fara ne lokacin da Henry ya roki ya gwada motar bayan an daidaita farashin a kan Naira miliyan 55.

Sai dai ya zarce da motar kuma tun daga lokacin ba a same shi ba.

Daga baya rundunar FCT ta bayyana Henry ya shiga hannu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Josephine Adeh ta shaidawa manema labarai a daren Laraba cewa, an gano motar a jihar Delta.

A cewarta, kwato motar da rundunar ‘yan sandan jihar Delta ta yi, “alama ne na hadin gwiwar ‘yan sanda a fadin ƙasa”.

“Hukumar ƴansandan FCT tun farko ta fara gudanar da bincike na gaskiya game da lamarin, kuma ta sanar da wasu Dokokin da suka kai ga gano motar,” inji ta.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp