fidelitybank

Ƴansanda na bincike kan mutuwar ƙananan yara biyar a cikin mota a Nasarawa

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Nasarawa ta ce ta fara bincike kan mutuwar wasu ƙananan yara biyar a garin Agyaragu cikin ƙaramar hukumar Obi a jihar.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar SP Ramhan Nansel, ya fitar yau Litinin a birnin Lafia.

Sanarwar ta ce an gano gawawwakin yaran ne a cikin lalatacciyar motar da ke ajiye a gidan wani Mista Abu Agyeme.

Ta ce tuni kwamishinan ‘yan sandan jihar Nasarawa, Shetima Jauro-Mohammed ya umarci gudanar da cikakken bincike don tabbatar da haƙiƙanin abin da ya faru.

A ranar Lahadi da misalin ƙarfe 5:30 na yamma ne, wani magidanci ya kai rahoto ga ‘yansanda cewa an gano ƙananan yara kwance shame-shame ba sa motsi a cikin wata lalatacciyar mota da ke yashe a harabar wani gida.

Yaran waɗanda shekarunsu suka kama daga shida zuwa goma, mata uku ne sai maza biyu kuma an tabbatar da rasuwarsu ne a asibitin Aro da ke garin Agyaragu sakamakon abin da ake zargi shaƙewar numfashi ce.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp