fidelitybank

Ƴanbindiga sun sace wanda ya lashe gasar karatun Al-Qur’ani ta Najeriya

Date:

Ƴanbindiga sun sace mutumin da ya zama zakaran gasar karatun al’qur’ani ta bana tare da danginsa a kan hanyar Faskari zuwa ƴankara a jihar Katsina.

Shugaban ƙaramar hukumar Faskari, Hon Musa Ado Faskari ya shaida wa BBC faruwar lamarin, inda ya ce ƴanbindigar sun sace Abdulsalam Rabi’u Faskari tare da mahaifinsa da ƴan’uwansa a lokacin da suke kan hanyar komawa gida bayan sun halarci fadar gwamnatin Katsina inda gwamna ya karrama gwarzon.

Hon. Musa Faskari ya ce gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda ne ya gayyaci , Abdulsalam Rabi’u Faskari tare da iyalansa ciki har da mahaifinsa a ƴan’uwansa, domin karrama shi bisa nasarar da ya samu ta zama gwarzon gasar karatun al-qur’ani da aka kammala a jihar Kebbi.

”A kan hanyarsu ta komawa gida ne, sun baro Funtua a kan hanyar Faskari zuwa ƴankara , ƴanbindiga suka tare su tare da yin garkuwa su duka, sai mutum guda da ya samu nasarar kuɓuta”, in ji shugaban ƙaramar hukumar.

Ya ce lamarin ya rutsa da aƙalla mutum bakwai – waɗanda duka dangin juna ne, sai abokin gwarzon gasar guda, wanda shi ma ya halarci taron karramawar.

Ya ƙara da cewa hukumomi na ci gaba da neman mutanen domin kuɓutar da su cikin ƙoshin lafiya.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp