An sace fasinjoji sama da ashirin a wasu motoci biyar a kan hanyar Mariga zuwa Kontagora da ke jihar Naija.
Shugaban majalisar dokokin jihar wanda kuma shi ne wakilin mazaɓar Mariga inda lamarin ya faru, Abdulmalik Sarkin-Daji ya tabbatar da labarin ga manema labarai, kamar yadda jaridar Dailt Trust ta ruwaito.
Ya ce ɓarayin sun datse hanyar ne ta Mariga zuwa Kontagora a shekaran jiya Alhamis a daidai titin Babbar-Lamba da Beri inda suka yi awon-gaba da fasinjojin.
Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martani kan yadda sojojin Najerya suka musanta labarin da ke cewa ɓarayin daji sun kama sansanin horonsu a yankin ƙaramar hukumar Kontagora, yankin da ya kai har Mariga.
Abdlmalik ya ce, iyalan waɗanda aka sace a baya suna kai wa ɓarayin dajin kuɗin fansa sau da dama a cikin dajin, wanda ya ce ɓangare ne na sansanin atisayen sojin.
Ya ce wasu daga cikin waɗanda ɓarayin ke garkuwa da su sun gaya wa ‘yan uwansu cewqa an tsare su ne dajin da ba shi da nisa da barikin soji na Kontagora.
Shugaban ya ce su ma waɗanda aka sace ranar Alahamis an kai su dajin ne, inda ya yi kira ga hukumomin sojin na Najeriya da su nemi bayanai na gaskiya su je su kawar da waɗannan ɓarayin daji.
Jariadr ta ce, kakakin rundunar ‘yansandan jihar ta Naija Wasiu Abiodun ya ce zai samo cikakken bayanin satar mutanen kafin ya yi magana amma kuma ba a ji shi ba.