fidelitybank

Ƴanbindiga sun kashe tare da sace kuɗaɗe a wani hari a Kebbi

Date:

Hukumomi da ga jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya sun tabbatar da mutuwar mutum guda tare da raunata wasu bayan da wasu ƴanbindiga suka kai hari garin Gulma da ke yankin aramar hukumar Argungu a jihar.

Shugaban ƙaramar hukumar Hon Aliyu Sani Gulma, ya shaida wa BBC cewa maharan sun shiga garin ne da misalin ƙarfe takwas na maraicen ranar Alhamis ɗaue da muggan makamai.

”Ƴanbindigar sun shiga garin ne a kan babura bakwai ɗauke da goyon bibbiyu, ciki har da mata biyu, ɗauke da muggan makamai, inda suka je wani babban kantin sayar da kayyaki na Alh Fatawu a garin, suka kuma buƙaci a ba su kuɗaɗe”.

Shugaban ƙaramar hukumar ya ce mata biyu daga cikin ƴanbindigar sun tsaya a ƙofar kantin, riƙe da bindigogi, yayin da sauran mazan suka shiga cikin domin ƙwato kuɗaɗe.

”Sun faɗa masu kantin cewa kuɗin Saifa suke ce ba naira ba, sa dai kuma a kantin babu saifar sosai, lamarin da ya sa suka riƙa bugun masu kula da kantin, inda daga baya suka kwashe duka kuɗaɗen da ke cikin kantin suka yi awon gaba da su”, a cewar shuagaban ƙaramar hukumar.

Ya ce maharan sun kuma kashe mutum guda a cikin al’ummar gari tare da raunata wasu a dama a lokacin da suka shiga garin.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp