Hukumomi da ga jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya sun tabbatar da mutuwar mutum guda tare da raunata wasu bayan da wasu ƴanbindiga suka kai hari garin Gulma da ke yankin aramar hukumar Argungu a jihar.
Shugaban ƙaramar hukumar Hon Aliyu Sani Gulma, ya shaida wa BBC cewa maharan sun shiga garin ne da misalin ƙarfe takwas na maraicen ranar Alhamis ɗaue da muggan makamai.
”Ƴanbindigar sun shiga garin ne a kan babura bakwai ɗauke da goyon bibbiyu, ciki har da mata biyu, ɗauke da muggan makamai, inda suka je wani babban kantin sayar da kayyaki na Alh Fatawu a garin, suka kuma buƙaci a ba su kuɗaɗe”.
Shugaban ƙaramar hukumar ya ce mata biyu daga cikin ƴanbindigar sun tsaya a ƙofar kantin, riƙe da bindigogi, yayin da sauran mazan suka shiga cikin domin ƙwato kuɗaɗe.
”Sun faɗa masu kantin cewa kuɗin Saifa suke ce ba naira ba, sa dai kuma a kantin babu saifar sosai, lamarin da ya sa suka riƙa bugun masu kula da kantin, inda daga baya suka kwashe duka kuɗaɗen da ke cikin kantin suka yi awon gaba da su”, a cewar shuagaban ƙaramar hukumar.
Ya ce maharan sun kuma kashe mutum guda a cikin al’ummar gari tare da raunata wasu a dama a lokacin da suka shiga garin.