‘Yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Yobe Desert Stars sun gamu da hatsarin mota a ranar Alhamis yayin da suke tafiya Birnin Kebbi domin buga gasar lig.
A cewar wani rahoto daga kungiyar ‘yan jarida ta Desert Stars, hatsarin da ya afku a Sokoto, ya yi sanadin kananan raunuka ga jami’ai uku da wasu ‘yan wasa, wadanda aka yi musu jinya a wani asibiti da ke yankin.
Kungiyar ta yi kira ga magoya bayanta da masu sha’awar kwallon kafa a Damaturu da su yi addu’ar samun sauki ga wadanda suka jikkata.
“Muna kira ga magoya bayanmu da dukkan masoya kwallon kafa da su kwantar da hankalinsu tare da yin addu’ar samun sauki ga wadanda suka jikkata a hadarin,” in ji kulob din.
Hadarin dai ya hada da wata babbar motar safa da ke jigilar ‘yan wasan da jami’ansu, saboda bas din kungiyar ba ta cikin tsari.
Kokarin jin ta bakin jami’ai a wurin da kuma Damaturu domin jin ta bakinsu ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.