Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, ta nada alkalan wasan Togo a wasan neman gurbin shiga gasar Olympics ta 2024 tsakanin Super Falcons ta Najeriya da Habasha.
Za a gudanar da gasar zagaye na biyu na share fage na gasar kwallon kafa ta mata ta Paris 2024 a filin wasa na Moshood Abiola, Abuja.
Kindedji Edoh za ta kasance a cibiyar kuma ‘yan uwanta, Agbedanu Abra Sitofe, Awutey Kossiwa Kayigan, da Amedome Vincentia Enyonam za su taimaka.
Oulare Daloba daga Guinea ne zai yi aikin tantance alkalan wasa, yayin da Ziga Christine Enyonam ‘yar Ghana za ta zama kwamishinan wasa a Abuja.
Super Falcons ta kasa samun tikitin shiga gasar Olympics karo uku da suka gabata.
‘Yan Afirka ta Yamma suna da kwarin gwiwa bayan sun tsallake zuwa zagaye na 16 a gasar cin kofin duniya ta mata ta FIFA ta 2023.