A yayin da babban zaben shekarar 2023 ke kara karatowa, gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, tare da wasu masu neman takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, sun yi wata ganawar sirri a birnin Fatakwal a ranar Laraba.
Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma mai fatan zama shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, bai halarci taron ba.
Mai taimaka wa gwamnan jihar ta Rivers kan harkokin yada labarai ya ce, wadanda suka halarci ganawar sirrin sun hada da gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Mohammed da gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.
Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, da tsohon manajan daraktan bankin kasa da kasa na FSB, Dr Mohammed Hayatu-Deen.