Uwargidan shugaban ƙasa, Aisha Buhari, ta bukaci jam’iyyun siyasa da su dauki mata a matsayin abokan takarar su ga ‘yan takarar da za su fafata a zabe a mukamai daban-daban a fadin kasar.
Aisha Buhari ta yi wannan magana ne a daren ranar Asabar, a lokacin da ta karbi bakuncin masu neman takarar shugaban kasa daga jam’iyyun siyasa daban-daban zuwa buda baki a watan Ramadan a fadar gwamnati da ke Abuja.
Aisha ta gayyaci daukacin masu neman shugabancin kasar nan, a dukkan jam’iyyun siyasa, zuwa buda-bakin watan Ramadan.
Wasu ‘yan takarar shugaban kasa, wadanda suka halarci taron, wanda aka gudanar a dakin taro na gidan gwamnatin, Abuja, sun hada da tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Tinubu; Gwamna Dave Umahi na Ebonyi; Gwamna Bala Mohammed na Bauchi; Ministan kwadago da samar da ayyuka Chris Ngige; Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, wanda tsohon gwamnan jihar Edo, Farfesa Oserheimen Osunbor ya wakilta.
Sauran manyan baki sun hada da, gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i; Ministan harkokin Neja Delta Godswill Akpabio; wanda ya taba zama shugaban jam’iyyar PDP na kasa Cif Barnabas Gemade; Tsohon kakakin majalisar wakilai Yakubu Dogara, da hamshakin mai da iskar gas, Tein Jack-Rich, sun halarci taron.