fidelitybank

Ƴan takara ku yi taka tsantsan a lamarin ku – Jonathan

Date:

Tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bukaci ‘yan takara da kuma sauran ‘yan siyasa a kan su rika taka-tsantsan a kan dorewar kasa da kuma sanya jin dadi da walwalar al’ummar kasar a gaba a yayin yaki neman zabe.

Goodluck Jonathan, ya yi wannan kira ne a ranar Alhamis a wajen taron shekara-shekara kan irin tariin da tsohon shugaban mulkin sojan kasar Ibrahim Badamasi Babangida ya kafa.

A cewarsa, yana da matukar muhimmanci ga ‘yan Najeriya su kawar da dukkan wasu bambance-bambancen da ke tsakaninsu, su shiga a dama da su a cikin harkokin siyasa don zabar shugabannin da za su kawo sauyi a kasar.

Ya ce,” Zabuka masu zuwa suna da matukar muhimmanci wajen ci gaban mu, a don haka ne nake jan hankalin ‘yan siyasa da su rinka taka-tsantsan wajen hada kai da kuma samar da zaman lafiya a kasa.”

Jonathan, ya ce a wannan lokaci da ake ciki bai kamata mu rinka nuna halin ko in kula da abubuwa da suka dace mu mayar da hankali a kai ba, dole mu sanya a ran mu cewa zamu shiga a dama damu a cikin harkokin siyasa.Dole kuma mu wayar wa da sauran ‘yan uwanmu kai a kan muhimmancin kada kuri’a a lokacin zabe.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp