A ranar Larabar da ta gabata ne jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanar da cewa, ta sayar da fom din takarar shugaban kasa 28, inda 25 daga cikinsu suka cike suka mayar da na su.
Felix Morka, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Kasa ne ya bayyana haka a lokacin da ya bayyana wa gidan Talabijin na Channels.
Sanata Chris Ngige, Ministan Kwadago, Samar da Aikin yi; Timipre Sylva, Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur; da Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin Najeriya na cikin wadanda suka gaza mika fom dinsu, a cewar jam’iyyar APC.
Ngige da Sylva sun bayyana cewa, sun janye daga takarar shugaban kasa a 2023, amma har yanzu gwamnan CBN bai bayyana aniyarsa ba.
Ya kuma garzaya kotu domin neman umarnin hana babban Atoni-Janar na kasa, da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa tilasta masa yin murabus daga mukaminsa idan yana son tsayawa takara a zaben 2023. Wannan addu’ar har yanzu ba a yi ba.
Morka ya ce, “Zan iya ba ku cikakken wannan bayanin saboda wasu da kuka ce sun yi watsi da su, sun yi hakan ne a fili amma har yanzu ba su sanar da jam’iyyar hakan a hukumance ba. Kuma waɗannan abubuwan ba lallai ba ne su faru a lokaci guda.