fidelitybank

Ƴan Sandan sun kashe riƙaƙƙen ɗan bindiga a Katsina

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Katsina, ta ce, ta daƙile wani hari da aka kai Magamar Jibiya da Ƙaramar Hukumar Jibiya duk a Jihar Katsina tare da kashe wani gawurtaccen ɗan bindiga.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sanda jihar SP Gambo Isah ya fitar, ƴan sandan sun ƙwace bindiga ƙirar AK 47 guda ɗaya da ƙundun harsasai guda huɗu da ke ɗauke da harsasai 90.

Ɗan bindigan da aka kashe sunansa Ibrahim Dangawo wanda ake zargin shi ya kitsa wani hari da aka kai har aka kashe wani tsohon DPO na Jibiya wato DSP Abdulkadir Rano.

A jiya Litinin da misalin huɗu da rabi na yamma ne ƴan bindiga suka rinƙa harbi kan mai uwa da wabi inda suka kai hari kan wani shingen binciken ƴan sanda a Magama a kwanar Hirji a kan hanyar Jibiya.

Bayan musayar wuta da ƴan sandan suka yi da su, a nan ne ƴan sandan suka daƙile harin tare da ƙwace wasu makamansu.

Sanarwar ta ce akasarin yan bindigan da suka tsira daga harin sun tsira da raunin harbin bindiga.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp