fidelitybank

Ƴan sandan Kaduna sun kama mai shekaru 20 da bindigogi

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ta ce, jami’anta sun kama wani dan bindiga mai shekaru 20 da haihuwa dauke da bindigogi kirar AK-47 guda biyu a unguwar Galadimawa da ke karamar hukumar Giwa a jihar.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mohammed Jalige, ya fitar a ranar Asabar da ta gabata, rundunar ‘Operation Restore Peace’ da ke aiki a kan sahihan bayanan sirri, sun tarwatsa wani kogon masu garkuwa da mutane da ke dajin Galadimawa, bayan sun yi artabu da ‘yan bindigar cikin wata mumunar bindiga.

A cewarsa, wasu ‘yan ta’addan sun garzaya dajin da raunuka daban-daban

Ya ce an kama daya daga cikin wadanda ake zargin Yusuf Monore dan shekara 20 dauke da bindigogi kirar AK 47/49 guda biyu da harsashi guda biyar masu rai 7.62 X 39mm da kuma wayoyin hannu, kuma a yanzu haka ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike.

Sai dai a halin yanzu jami’an na kan bin diddigin wadanda ake zargi da gudu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kaduna, Yekini Ayoku, ya yabawa irin rawar da jami’an suka nuna tare da bada tabbacin zurfafa hadin kai da hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro a jihar.

Hakazalika, CP ya kuma bukaci ‘yan kasa da mazauna jihar Kaduna masu bin doka da oda da su kasance masu lura a kodayaushe tare da kai rahoto ga jami’an tsaro cikin gaggawa, tare da ba su tabbacin sirrin duk wata hanyar samun bayanai.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp