fidelitybank

Ƴan sanda sun kama matar da ake zargi da kashe kishiyarta a Katsina

Date:

Ƴan sanda a jihar Katsina sun kama wata matar aure da ake zargi da kashe kishiyarta.

Lamarin ya faru ne a bayan wata makarantar firamare ta Dadi da ke unguwar Sabon Gari, a ƙaramar hukumar Daura bayan da wata matsala ta cikin gida tsakanin matan auren biyu ta rikiɗe zuwa rikici mai muni da ya kai ga mutuwa.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya fitar a ranar Lahadi, inda ya bayyanawa manema labarai abin da ya faru.

Sanarwar ta ce: “A ranar 24 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 11 na dare ne ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari suka samu rahoto daga wani Nasir Yusuf, mijin matar, cewa ya dawo gida daga kasuwa ya tarar da matarsa ta farko mai suna Zainab Lawal tana kwance cikin jini, an caka mata wuƙa sau da dama.”

“Da samun rahoton, DPO na yankin tare da tawagar jami’ai suka garzaya wurin da abin ya faru, inda suka gaggauta kai matar zuwa asibitin koyarwa na tarayya da ke Daura domin ceto rayuwarta, amma likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da rasuwarta.”

“A yayin bincike ne aka kama kishiyarta, Rabi’a Labaran, wadda suke zaune a gida ɗaya bisa zargin aikata kisan.” in ji sanarwar.

“Kishiyar dai ta amsa laifin cewa ita ta aikata kisan bayan wani saɓani da ya shiga tsakaninsu da mamaciyar, wanda ya rikiɗe zuwa fada har ta kai ga wannan mummunan lamari” sanarwar ta ƙara da cewa.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Bello Shehu, ya gargaɗi jama’a da su nisanci tashin hankali a cikin gida da kuma gujewa ɗaukar doka a hannu.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp