fidelitybank

Ƴan sanda sun kama masu safar ƙananan yara a Abuja

Date:

Rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja ta kama wani mutum da take zargi da safarar ƙananan yara kimanin 12 a cikin mota zuwa jihar Ogun.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce ta kama mutumin ne ranar Juma’a da rana a lokacin da yake safarar ƙananan 12 da suka haɗar da mata takwas da maza huɗu a cikin mota a kan hanyarsa ta zuwa wani wuri a jihar Ogun da ke kudancin ƙasar.

Sanarwar ta ce binciken farko ya nuna cewa ƙananan yaran ‘yan tsakanin shekara biyar zuwa 16, dukkansu ‘yan asalin ƙaramar hukumar Akwanga ne daga jihar Nasarawa da ke tsakiyar Najeriya.

‘Yan sandan sun zargi wani fasto mai suna Simon Kado da wani mutum guda – waɗanda ta ce suna hannunsu – da hannu a safarar yaran zuwa jihar ta Ogun wa.

Rundunar ‘yan sandan Abujan ta ce tana tuntuɓar takwararta da ke jihar Nasarawa domin shirya yadda za a mayar da yaran wajen danginsu.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp