Wani hargitsi ya tashi da yammacin ranar Laraba, lokacin da dandazon magoya bayan jam’iyyar NNPP suke gudanar da zanga-zanga a jihar Kano, dangane da hukuncin kotun daukaka kara da soke nasarar Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Ƴan sanda sun tare masu zanga-zangar wadanda suka yi yunkurin zuwa gadar Kofar Nassarawa, bayan sun gudanar da wani taron addu’o’i a filin Kofar Dan’agundi.
Hotuna a kafofin sada zumunta sun nuna yadda aka kona tayoyi a kan titin zuwa Jami’ar Bayero, lamarin da ya kawo tsaiko ga masu ababen hawa.
Haka zalika, an yi jefe-jefe a lokacin hargitsin, ‘yan sanda kuma sun harba hayaki mai sa hawaye.
Bayanai sun ce an kama wasu daga cikin masu zanga-zangar, sannan an ga karin ‘yan sanda a kan titin zuwa gidan gwamna.
Daga bisani dai, kurar ta lafa.
Magoya bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf da jam’iyyarsa ta NNPP sun yi kiran gudanar da abin da suka ce “taron addu’o’i” ne don nuna adawarsu ga hukuncin kotun daukaka kara wanda tun farko ya bai wa Nasiru Yusuf Gawuna nasara na jam’iyyar APC.
Kotun wadda ta yi zamanta a ranar Juma’a 17 ga watan Nuwamba, ta yanke hukuncin cewa Abba Kabir Yusuf ba dan jam’iyya ba ne, don haka bai cancanci tsayawa takara ba.
Sai dai, bayan fitar da kwafin takardar cikakken hukuncin a ranar Laraba, takaddama ta sake barkewa, inda ‘yan jam’iyyar NNPP ke da’awar cewa su ma hukuncin ya ba su nasara a kan abokan kararsu