fidelitybank

Ƴan Sanda sun harba borkonan Tsohuwa a kan magoya bayan NNPP a Kano

Date:

Wani hargitsi ya tashi da yammacin ranar Laraba, lokacin da dandazon magoya bayan jam’iyyar NNPP suke gudanar da zanga-zanga a jihar Kano, dangane da hukuncin kotun daukaka kara da soke nasarar Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Ƴan sanda sun tare masu zanga-zangar wadanda suka yi yunkurin zuwa gadar Kofar Nassarawa, bayan sun gudanar da wani taron addu’o’i a filin Kofar Dan’agundi.

Hotuna a kafofin sada zumunta sun nuna yadda aka kona tayoyi a kan titin zuwa Jami’ar Bayero, lamarin da ya kawo tsaiko ga masu ababen hawa.

Haka zalika, an yi jefe-jefe a lokacin hargitsin, ‘yan sanda kuma sun harba hayaki mai sa hawaye.

Bayanai sun ce an kama wasu daga cikin masu zanga-zangar, sannan an ga karin ‘yan sanda a kan titin zuwa gidan gwamna.

Daga bisani dai, kurar ta lafa.

Magoya bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf da jam’iyyarsa ta NNPP sun yi kiran gudanar da abin da suka ce “taron addu’o’i” ne don nuna adawarsu ga hukuncin kotun daukaka kara wanda tun farko ya bai wa Nasiru Yusuf Gawuna nasara na jam’iyyar APC.

Kotun wadda ta yi zamanta a ranar Juma’a 17 ga watan Nuwamba, ta yanke hukuncin cewa Abba Kabir Yusuf ba dan jam’iyya ba ne, don haka bai cancanci tsayawa takara ba.

Sai dai, bayan fitar da kwafin takardar cikakken hukuncin a ranar Laraba, takaddama ta sake barkewa, inda ‘yan jam’iyyar NNPP ke da’awar cewa su ma hukuncin ya ba su nasara a kan abokan kararsu

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp