Dakarun rundunar ƴan sanda sun daƙile harin wasu da ake zargin ƴan ta’adda ne a wani kauye dake kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da kakakin hukumar yan sandan Kaduna, DSP Muhammad Jalige, ya fitar, kamar yadda talabijin ta rawaito.
A cewar kakakin yan sandan, jami’ai sun kai ɗauki ne kan rahoto fasaha da suka samu, inda suka ga ‘yan bindigan adadi mai yawa a kusa da ƙauyen Kurmin Kare dake kan hanyar Abuja-Kaduna a karamar hukumar Chikun.
Ya ce, ƴan ta’addan sun taho da nufin aiwatar da wani mummunan nufin su zuwa wani wuri da ba’a sani ba, amma yan sanda suka fatattake su da karfin tsiya.