fidelitybank

Ƴan sanda sun damƙe mutane 781 lokacin zaɓe

Date:

Rundunar ‘yan sanda, ta ce, ta kama mutum 781, kan laifukan da suka shafi zaɓe a lokacin zaɓukan ƙasar nan.

Babban sifeton ‘yan sandan ƙasar Usman Baba Alkali ne ya bayyana haka ranar Litinin a lokacin da yake ganawa da kwamishinonin ‘yan sanda na jihohin ƙasar 36, tare da wasu manyan jami’an ‘yan sandan.

Karanta Wannan: Siyasa na neman wargaza kan ƴan Najeriya – Sarkin Yarbawa

Yayin da yake cikakken bayani game da kamun, Baba Alkali ya ce an aikata laifukan zaɓe 145 a lokacin zaɓen shugaban ƙasa, inda rundunar ta kama mutum 203.

Sai kuma a lokacin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisun dokokin jihohi inda rundunar ta ce an aikata laifuka 304, lamarin da ya sa rundunar ta kama mutum 578.

Babban sifeton ‘yan sandan ya ce rundunar ta shirya ganawa babban sifeton da kwamishinonin ‘yan sanda na jihohin ƙasar da kuma sauran manyan jami’an ‘yan sandan, don tattauna barazanar da tsaron ƙasar ke fuskanta.

Wanda a cewarsa ‘yan siyasa ke ƙoƙarin tayar da hatsaniya a ƙasar bayan zaɓukan ƙasar da suka gabata.

Ya kuma yi Allah wadai da ‘yan siyasar da suke ƙoƙarin tayar da hargitsi ta hanyar tunzura jama’a domin cimma wasu muradunsu.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp