fidelitybank

Ƴan sanda sun ƙara kashe masu zanga-zanga a Kenya

Date:

Wasu ƙarin mutum hudu ne ake zargin ‘yan sandan Kenya sun kashe yayin zanga-zangar adawa da gwamnatin shugaba William Ruto a jiya, wanda ya kawo adadin waɗanda suka mutu sama da 50 a cikin watan da ya gabata, kamar yadda NTV ta ruwaito.

Mutuwar ta faru ne a gundumar Makueni, Nairobi, da Kitengela.

Hukumar kare haƙƙin bil adama ta ƙasar Kenya ta bayar da rahoton cewa, mutum 50 ne suka mutu tun bayan fara zanga-zangar a ranar 18 ga watan Yuni.

Muƙaddashin Sufeto Janar na ‘yan sandan ƙasar Douglas Kanja ya yi gargadin yiwuwar kutsawar masu aikata muggan laifuka a zanga-zangar, lamarin da ya sa ‘yan sanda suka mayar da martani mai karfi da hayaƙi me sa hawaye da barbi da harsasai.

Mutane da dama a kananan hukumomin Nakuru da Nairobi da Mombasa da Nyeri da kuma Machakos sun jikkata.

Ƙungiyar ‘yan jarida ta Kenya (KUJ) ta yi kira da a gudanar da bincike a kan wani dan sanda da ya harbe wani dan jarida da ke bayar da rahoto kan zanga-zangar a gundumar Nakuru.

Duk da janye dokar ƙrin harajin da shugaba Ruto ya yi, da rage kashe kudade, da kuma rusa majalisar ministocinsa, masu zanga-zangar na ci gaba da nemansa ya yi murabus, bisa la’akari da cin hanci da rashawa da rashin shugabanci na gari.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp