Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, ta bayyana cewa tana neman Owodunni Ibrahim wanda aka fi sani da Primeboy, biyo bayan rashin amsa gayyatar ‘yan sanda.
An gayyaci Primeboy ne a yayin da ake gudanar da bincike kan lamarin da ya kai ga mutuwar Ilerioluwa Aloba aka Mohbad.
Wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in ‘yan sandan Legas, Benjamin Hundeyin, ta kara da cewa: “Ibrahim tsayinsa kusan 1.64-m, namiji ne, duhu ne mai hade da alamomin kabilanci sannan kuma Yarbawa a kabila. Adireshin sa na ƙarshe shine 3rd Power, Oke Eletu, Ikorodu.
“Idan an gani, a tuntubi ofishin ‘yan sanda mafi kusa ko a kira lambar waya 0803 688 5727.
“Kwamishanan ‘yan sanda reshen jihar Legas, CP Idowu Owohunwa, yana bayar da tukuicin kyautar N1,000,000 (Naira Miliyan Daya Kadai) ga duk wanda ya samu bayanai masu amfani da zai kai ga kama shi.”
Wannan dai na zuwa ne kwana guda bayan da mawakin Najeriya, Azeez Fashola, wanda aka fi sani da Naira Marley, ya dawo kasar don “taimakawa” a binciken da ake yi na mutuwar tsohon dan wasan sa.