fidelitybank

Ƴan Sanda na amfani da ƙarfin wuce ƙima a kan masu zanga-zanga – Ƙungiyar Kare Hakkin Ɗan Adam

Date:

Kungiyar marubuta ta masu rajin kare hakkin ɗan Adam a Najeriya, HURIWA, ta soki ‘yansandan kasar nan kan yadda suke amfani da karfin da ya wuce kima da kuma makamai a kan masu zanga-zangar da ake yi a Najeriya, wadda ta shiga kwana na uku.

A sanarwara da kungiyar ta fitar ta hannun shugabanta Emmanuel Onwubiko, ta ce yadda ‘yansanda ke tunkarar masu zanga-zangar ta lumana a rana ta uku, ko kadan babu kwarewa da nuna mutuntaka, kuma mugun laifi suke aikatawa.

Kungiyar ta nuna damuwa kan yadda ta ce ‘yansandan sun kama mutane da dama da suka taru a babban filin wasa na kasar da ke Abuja,Moshood Abiola Stadium, domin ci gaba da zanga-zangarsu ta lumana a yau Asabar.

Kungiyar ta yi gargadin cewa mummunan matakin da ‘yansandan ke dauka a kan masu zanga-zangar idan ba a ga illarsa ba yanzu to a nan gaba za a gani, abin da zai biyo baya.

Haka kuma ta ce idan ba a fito da ‘yansandan da suka harbi masu zanga-zanga ba an gurfanar da su gaban shari’a, tare da hukunta su kamar yadda doka ta tanada, lamarin zai iya sake janyo zanga-zangar da aka yi ta neman kawo karshen cin zalin da ‘yansanda ke yi wato #ENDSARS.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp