fidelitybank

Ƴan Sanda ku taka wa Abba Gida-Gida birki – Abdullahi Abbas

Date:

Shugaban jam’iyyar APC a Kano, Abdullahi Abbas, ya bukaci rundunar ‘yan sanda da ta kama tare da gurfanar da dan takarar gwamna na New Nigeria, NNPP, Abba Kabir Yusuf, bisa zarginsa da kawo ‘yan bangar siyasa.

Abbas, ya ce Yusuf ya mayar da gidan kakanninsa ya zama gidan ‘yan banga na siyasa, inda suke tafka muggan kwayoyi da sauran miyagun ayyuka.

“A yanzu haka, mutane da yawa suna ƙaura daga yankin saboda fargabar rashin tabbas saboda ba za su iya rayuwa da ‘yan baranda ɗauke da manyan makamai kuma a kodayaushe suna shan muggan kwayoyi, shi ya sa ‘yan sanda suka yi gaggawar shiga lamarin,” in ji Abdullahi Abbas.

Ya ce, lamarin idan ba a kama shi kan lokaci ba, zai bude wata kofa ta munanan barazanar tsaro ganin zaben 2023 na gabatowa.

Sai dai da yake mayar da martani kan zargin, kakakin dan takarar gwamnan jihar a karkashin jam’iyyar NNPP, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya ce zargin ba shi da tushe balle makama, sai dai shugaban jam’iyyar APC shi ne ake son gabatar da kansa a gaban hukumomin tsaro saboda kalamansa na rashin zaman lafiya da kalaman kiyayya.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...

Kano na cikin jihohin da ba su yi katin zabe sosai ba – INEC

Bayanan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya...

Mun gano filin wasa na Sani Abacha ba shi da inganci – NPFL

Hukumar shirya gasar cin kofin kwararru ta kasa (NPFL),...

Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya ya fadi

Jirgin ƙasa ɗauke da fasinjoji da ya taso daga...

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...
X whatsapp