fidelitybank

Ƴan Sanda Adamawa sun yi holin mutane 38

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa a ranar Talata ta yi holin wasu mutane 38 da ake zargi.

Wadanda ake zargin dai suna tsakanin shekaru 16 zuwa 60 ne. Ana tuhumar su da laifin yin garkuwa da mutane, fashi da makami, fyade, kisan kai da sauran laifuka.

Rundunar ta ce an kama wadanda ake zargin ne a kananan hukumomin Fufore da Yola ta Arewa da kuma Girei biyo bayan aiwatar da aikin sa ido da jami’an suka yi bisa alkawarin da rundunar ta dauka na kawar da miyagun laifuka a jihar.

Da yake zantawa da manema labarai yayin gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar ‘yan sanda da ke Yola, kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Sikiru Akande, ya ce an kama wadanda ake zargin ne a cikin makon da ya gabata.

“Ina farin cikin gayyatar ku a yau Talata, 9/8/2022 a ofishin ‘yan sanda na jihar tare da gabatar muku da gaggarumar nasarorin da rundunar ta samu a cikin makon da ake nazari a kai,” in ji CP.

Ya lissafa kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin kamar bindiga kirar AK-47, Bindigo guda 1 na gida, Keke NAPEP guda 1, Laptop guda uku, DVD 1, stabilizer 1, wayoyin GSM guda 8, katin SIM na GSM da yawa, magunguna iri-iri, daga cikin su. wasu.

DAILY POST ta rahoto daga wani bincike mai zaman kansa cewa an yi wa wani farfesa na Jami’ar Moddibo Adama da ke Girei, Yola fashi a dakinsa na jami’ar a daren ranar Lahadin da ta gabata.

Daga cikin kayayakin da aka kwaso daga gidansa har da Laptop guda uku da wayoyi takwas na Farfesa Abdulkadir Raji da na iyalansa.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp