fidelitybank

Ƴan Sanda a Zamfara sun kuɓutar da mutane 17

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ta kubutar da mutum 17 da aka yi garkuwa da su a dazukan Gando, da Bagega da kuma dajin Sunke a karamar hukumar Anka da ke jihar

A wata sanarwa da mai magana da rundunar ‘yan sandan jihar Mohammed Shehu ya sanya wa hannu, ya ce an sace mutanen ne a kauyukan Akawa da Gwashi da Tungar Rogo da kuma Anka, inda aka kai su sansanin ‘yan ta’adda da ke cikin dazukan.

Sanarwa ta ci gaba da cewa “Rundunar ta kubutar da mutanen ne bayan da jami’an tsaron suka samu bayanan da ke cewa wasu gungun ‘yan ta’adda sun kai farmaki wadannan kauyuka tare da sace mutane masu yawa, inda kuma suka tafi da su cikin dazukan Gando, da Bagega da kuma dajin Sunke”

Mutanen dai sun kwashe kusan mako guda a hannun ‘yan fashin dajin kamar yadda sanarwar ta bayyana.

A baya-bayan nan dai Jihar Zamfara na fuskantar karuwar hare-haren ‘yan fashin daji wadanda ke sace mutane domin neman kudin fansa.

Ko a makon da yabata ma dai ‘yan fashin dajin sun yi harbi kan mai uwa-da-wabi ga mutanen da suka je cin kasuwa a Tashar ‘Yar Sahabi cikin yankin Ƙaramar Hukumar Maru ta Jihar , inda suka kashe mutum tara, tare da raunata mutum biyar ciki har da mata da kananan yara.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp