fidelitybank

Ƴan Najeriya sun nemi shugaban ƙasar Afrika ta Kudu ya kare su daga kai harin ƴan ƙasar

Date:

‘Yan Najeriya mazauna ƙasar Afirka ta Kudu, sun bukaci shugaban kasar, Cyril Ramaphosa da ya kare su da dukiyoyinsu daga hare-haren kyamar baƙin haure.

Al’ummar Najeriya mazauna kasar, sun yi wannan bukata ne a daidai lokacin da ake fama da tashe-tashen hankula da ake yi wa ‘yan kasashen waje a kasar Afirka ta Kudu.

Al’ummar Najeriya karkashin inuwar kungiyar ‘Nigerian Union South Africa’ (NUSA), sun gabatar da bukatar a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban NUSA, Mista Collins Mgbo da kuma sakon email daga Pretoria na kasar Afirka ta Kudu.

Ya ce, “Ina kira ga Shugaba Cyril Ramaphosa da ya taimaki al’ummarmu a wannan mawuyacin lokaci domin kada mu sake rasa ‘yan uwanmu a hare-haren kyamar baki.” in ji Mgbo.

Shugaban NUSA ya ce, ‘yan kasashen waje sun kara damuwa lokacin da kungiyar sama da mutane 2,000 suka gudanar da zanga-zangar nuna adawa da ma’aikatan bakin haure a wani bangare na “Operation Dudula”.

Dudula, kalmar Zulu wacce ke nufin “kore baya”, ta sami karbuwa a matsayin alamar haɓakar ƙiyayyar baƙi a Afirka ta Kudu, ƙasar da ta ga matakin rashin aikin yi ya ta’azzara kuma talauci ya ƙara tsananta ta hanyar Coronavirus.

“Rundunar ‘Operation Dudula’ ta fito da wasu daruruwan mutane a cibiyar ‘yan ci-rani da ke garin Soweto na kasar Afirka ta Kudu, tare da marasa aikin yi, dauke da makamai da kuma fusata da ‘yan kasashen waje da suka zarga da karbar ayyukansu, suna rera wa ‘yan kasashen waje ku koma gida. A cewar Mgbo.

Ya yi bayanin cewa NUSA ta damu da tsaron lafiyar ‘yan Najeriya a Afirka ta Kudu lokacin da kungiyoyin suka fara cin zarafi ba bisa ka’ida ba tare da lalata kadarori da kasuwanci na ‘yan kasashen waje, musamman ‘yan Najeriya.

“Mun damu saboda a baya zanga-zangar kyamar baki ta haifar da tashin hankali da sace-sacen shagunan ‘yan kasashen waje.

A shekarar 2008, harin da aka kai wa ‘yan kasashen waje ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 62, kuma a shekarar 2015, an kashe ‘yan’uwa ‘yan Afirka bakwai da ba su ji ba ba su gani ba. In ji jaridar Guardian.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp