Jigo a jam’iyyar APC na kasa, Asiwaju Bola Tinubu, a jiya, ya bayyana cewa ‘yan Najeriya sun gaji da uzuri da koke-koke a baya, wadanda suka hada da rashin tsaro, da samar da wutar lantarki, ‘yan fashi da kuma tabarbarewar tattalin arziki da suka dabaibaye ƙasar.
Tinubu ya bayyana haka ne a wajen wani gagarumin gangamin da matasa sama da 40,000 suka gudanar a karkashin inuwar kungiyar cigaban matasa na Kudu maso Yamma wato Progressive Youth of South-West, domin bayyana goyon bayansu ga kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa da ya wakana a Mobolaji Johnson Arena, Onikan, Legas.
Matasan da suka fito daga jihohin Legas da Ogun da Osun da Ekiti da Ondo da kuma Oyo sun hallara a Legas da yawan gaske, domin nuna goyon bayansu ga burin shugaban jam’iyyar na kasa.
Tinubu, a lokacin da yake jawabi ga matasan da ke cin karo da juna, ya bukace su da su hada kai da shi, domin sauya labarin Najeriya.
Ya ce: “Duk abin da kuke buƙata shi ne ƙarfin hali, ƙuduri da kuma juriya. Idan YouTube kadai yana da mutane biliyan 2.9 suna binsa, gami da duk ku da kuke tsaye a nan, to Najeriya za ta iya yin fice. Za mu iya yin shi, dole ne ku haɓaka halin iya-yi; dole ne ku yarda cewa kasar nan taku ce kuma kuna son canza labarin. Dole ne ku canza labarin yiwuwar, labarin ‘yan fashi; dole ne ku canza labarin kabilanci.
“Yan Najeriya, lokaci ya yi, muna da isassun iskar gas da za mu yi wutar lantarki da wadata sauran kasashen Turai don samun kudi. Kun san shi. Ba ma so mu gundure ku da shi. A lokacin da na fara, mun kasance muna tsintar gawa a kan tituna, amma a yau Legas tana daya daga cikin mafi tsafta, mafi samun ci gaba a kasar nan”. A cewar Tinubu
Tinubu ya bukaci matasan da su sake sabunta katin zabe na dindindin (PVCs), sannan su kasance a shirye su kada kuri’a a zaben 2023 mai zuwa.