fidelitybank

Ƴan Najeriya na cikin mawuyacin hali a Ukraine

Date:

Wasu dalibai ‘yan Najeriya da suka makale a birni Kherson na Ukraine wanda sojojin Rasha suka yi wa kofar rago sun bayyana mawuyacin halin da suka fada bayan mako biyu suna buya a wani dakin karkashin kasa.

Daliban na bukatar kasarsu ta dauki matakin ceto su da gaggawa.

Jerry Kenny ya shaida wa BBC cewa, shi da wasu abokansa shida ba su da lafiya, saboda mummunan halin da suke rayuwa cikinsa a dakin karkashin kasa, kuma ya ce ba su da abinci da sauran abubuwan more rayuwa.

“Wasu cikinmu ma ba sa iya magana saboda fargaba,” inji shi, kuma ya ce gwamnatin Najeriya “ba ta tuntube mu ba da zummar samar mana da ruwa da abinci”.

“Na yi magana da wakilan kasarmu da jakadu da kuma jami’an ma’aikatar harkokin waje kan yadda za a iya kwashe mu daga nan. Amma har yanzu babu labari.”

Ministan harkokin wajen Najeriya Geoffrey Onyeama ya ce, ya tuntubi jakadun Najeriya da ke Ukraine da Rasha, kuma sun tuntubi takwarorinsu na Rasha da na Indiya, domin samar da hanyoyin kwaso daliban daga Ukraine zuwa Najeriya.

Rahotanni na cewa har yanzu akwai daliban nahiyar Afirka fiye da 100, yawancinsu daga Najeriya da ke Kherson.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp