fidelitybank

Ƴan majalisa sun gayyaci shugaban jami’ar Dutsin-Ma kan rashin iya shugabanci

Date:

Kwamitin majalisar wakilai da ke kula da korafe-korafen jama’a ta gayyaci shugaban Jami’ar Tarayya ta Dutsin-Ma da ke jihar Katsina, Farfesa Armayau Hamisu Bichi da ya bayyana gabanta domin amsa tambayoyi kan zargin ‘rashin iya jagoranci’ da ake yi masa.

Gayyatar tasa ta biyo ne bayan wani mai suna Shehu Abubakar Tadda ya shigar da korafi kan yadda Farfesa Bichi yake tafiyar da salon shugabancinsa wanda bai dace ba, a cewarsa.

Kwamitin ya buƙaci shugaban jami’ar da ya bayyana gabansa a ranar Laraba 18 ga watan Satumban 2024.

Sanarwar ta ce ko da bai bayyana gaban kwamitin ba, za a iya ci gaba da sauraron batun a bayansa.

Majalisar wakilan ta ce gayyatar na a sashe na 88 da kuma 89 na kundin mulkin Najeriya, wanda ya ba ta damar bincike kan batutuwa da suka shafi al’umma.

Haka kuma, majalisar ta buƙaci wanda ya shigar da korafin Shehu Abubakar Tadda da shi ma ya bayyana gabanta.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp