fidelitybank

Ƴan Majalisa ne ke tallafawa Matasa ta ɓangaren shaye-shaye – Kawu Sumaila

Date:

Sanata Kawu Sumaila mai wakiltar Kano ta kudu a majalisar dattawa, ya zargi ƴan siyasa, musamman ƴan majalisa da ƙarfafa shaye-shayen ƙwayoyi a tsakanin matasa.

Ya ce ƴan siyasa suna sayo wa matasan ƙwayoyi, sannan suna ƙarfafa musu gwiwar ta’ammuli da su domin samun damar yi musu dabar siyasa musamman a lokacin zaɓe, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Kawu ya yi wannan jawabin ne a lokacin da yake nasa bayanin a kan ƙudurin da Sanata Rufa’i Hanga mai wakiltar Kano ta tsakiya ya gabatar, mai taken, “dokar kafa cibiyar hana shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da gyara tunanin mashaya da sauran abubuwa masu alaƙa,” a yau Talata.

“Yanzu da nake wannan maganar, yawancin ofisoshinmu da gidajenmu ba za a rasa ƙwayoyi ba,” in ji Kawu.

“Na san wasu jagororin siyasa da suke ƙarfafa gwiwar masu shaye-shaye a Najeriya. Don haka akwai buƙatar mu ɗauki wannan batu da muhimmanci.”

Ya ƙara da cewa, “mutum nawa ne a cikinmu za su iya rantse wa Ƙur’ani ko Baibul cewa ba sa ƙarfafa wa masu shaye-shaye a mazaɓunsu?”

A ƙarshe ya yi kira da a riƙa yin gwajin shaye-shaye ga duk wani wanda yake son tsayawa takara.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp