Mazauna garuruwan da ke kan iyakokin Najeriya da aka rufe na ci gaba da bayyana farin cikinsu, bayan da Buhari ya buɗe iyakokin da ke kan tudu a ranar Litinin.
Hukumar hana fasa-ƙwauri ta ce, gwamnatin tarayya ce ta ba da umarnin buɗe iyakokin huɗu a ƙarshen makon jiya.
An dai amince a bude iyakokin Idoroko a jihar Ogun da Jibiya dake jihar Katsina sai kuma iyakar Kamba a Kebbi da kuma iyakar Ikom a jihar Cross River.
Bayan bude iyakar Jibiya a Katsina, mutanen da ke yankin sun bayyana jin dadinsu kasancewar harkokin kasuwanci zai farfado a cewarsu.
Alhaji Salisu O I Jibiya, ya shaida wa BBC cewa, bude iyakokin nan ya sanya su cikin jin dadi da raha saboda sun shafe shekaru uku suna rufe abin da ya sanya su cikin takura.
Ya ce, duk da ka’idojin da hukumomi suka gindaya musu na irin abubuwan da za a rinka safararsu ta iyakokin, su kam sai san barka, saboda ko ba komai za su ci gaba da kasuwancinsu da suka jima basu yi ba.