Karamin Ministan Harkokin Waje, Ambasada Zubairu Dada, ya bukaci ‘yan jarida a kasar da su tabbatar da rage karuwar labaran karya a Najeriya.
Ministan ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake jawabi a makon manema labarai na shekarar 2022 da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya, NUJ ta shirya a jihar Neja.
Dada ya yi nuni da cewa, akwai bukatar ‘yan jarida su yi aiki tukuru na magance yada labaran karya domin akwai masu cimma muradun kansu.
Ya kuma kara da cewa, akwai bukatar hadin kan ‘yan kasar idan har ana son al’ummar kasar su yi nasara.
A nasa jawabin gwamnan jihar Neja Alh Abubakar Sani Bello wanda sakataren gwamnatin jihar Neja Ahmed Ibrahim Matane ya wakilta ya bayyana cewa, labaran karya ne suka sa al’ummomi da dama suka koma matsuguni.
“Hakan ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyi kuma dole ne a magance wannan lamarin sosai kuma gwamnatin jihar Neja tare da hadin gwiwar gwamnatin tarayya, suna yin duk mai yiwuwa don tabbatar da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi cikin kankanin lokaci,” in ji shi. .