fidelitybank

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Date:

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa a ƙirji da ’yan daba suka yi a kofar gidan tsohon shugaban karamar hukumar Dala, Ibrahim Dan Isle, da ke Bachirawa, titin Sakatariya, layin Dan Isle.

Arewa Update ta rawaito cewa, Dan uwan marigayin, Abubakar Mahmud, ya shaida wa Arewa Updates cewa Ibrahim mabiyin tsohon shugaban karamar hukumar ne a siyasa, daga baya suka ɓaɓe, sai a baya-bayan nan suka shirya.

Ya ce Dan Islen ne ya gayyace shi gida domin karɓar naman Sallah, kuma da ya je ƙofar gidan ya kira shi a waya ya sanar da shi yana dakon fitowarsa, sai wasu ’yan daba suka afka masa inda suka soke shi a ƙirji abin da ya yi ajalinsa.

Ya ƙara da cewa sun je ofishin ’yan sanda na Bachirawa inda suka taho ƙafa da ƙafa da DPO domin bincike, amma abin bai yiwu ba, domin Dan Isle ya kwashe iyalinsa ya gudu daga unguwar, ya rufe gidansa, a cewar Abubakar.

’Yan uwan marigayin sun nemi hukumomi su yi bincike na adalci a kan lamarin.

Dangane da wannan alʼamari dai Arewa Updates ta yi ta kiran wayar Dan Isle amma wayarsa na nuna ʼbusyʼ, sai dai mun aika masa da saƙon kar-ta-kwana amma shiru babu amsa.

To amma muna ci gaba da jira, in ya magantu za mu sanar muku.

Ko a watan Mayun da ya wuce dai, Kansilan Mazabar Gobirawa a Dala, Hon. Ibrahim Danwaire, ya zargi Shugaban Karamar Hukumar Dala, Hon. Surajo Ibrahim Imam, da shirya masa wata kitimurmura inda aka lakada masa dukan tsiya a sakatariyar karamar hukumar, sai da kyar ya sha.

Sai dai shugaban karamar hukumar ya musanta wannan zargin. Inji Arewa Update.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp