fidelitybank

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Date:

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa a ƙirji da ’yan daba suka yi a kofar gidan tsohon shugaban karamar hukumar Dala, Ibrahim Dan Isle, da ke Bachirawa, titin Sakatariya, layin Dan Isle.

Arewa Update ta rawaito cewa, Dan uwan marigayin, Abubakar Mahmud, ya shaida wa Arewa Updates cewa Ibrahim mabiyin tsohon shugaban karamar hukumar ne a siyasa, daga baya suka ɓaɓe, sai a baya-bayan nan suka shirya.

Ya ce Dan Islen ne ya gayyace shi gida domin karɓar naman Sallah, kuma da ya je ƙofar gidan ya kira shi a waya ya sanar da shi yana dakon fitowarsa, sai wasu ’yan daba suka afka masa inda suka soke shi a ƙirji abin da ya yi ajalinsa.

Ya ƙara da cewa sun je ofishin ’yan sanda na Bachirawa inda suka taho ƙafa da ƙafa da DPO domin bincike, amma abin bai yiwu ba, domin Dan Isle ya kwashe iyalinsa ya gudu daga unguwar, ya rufe gidansa, a cewar Abubakar.

’Yan uwan marigayin sun nemi hukumomi su yi bincike na adalci a kan lamarin.

Dangane da wannan alʼamari dai Arewa Updates ta yi ta kiran wayar Dan Isle amma wayarsa na nuna ʼbusyʼ, sai dai mun aika masa da saƙon kar-ta-kwana amma shiru babu amsa.

To amma muna ci gaba da jira, in ya magantu za mu sanar muku.

Ko a watan Mayun da ya wuce dai, Kansilan Mazabar Gobirawa a Dala, Hon. Ibrahim Danwaire, ya zargi Shugaban Karamar Hukumar Dala, Hon. Surajo Ibrahim Imam, da shirya masa wata kitimurmura inda aka lakada masa dukan tsiya a sakatariyar karamar hukumar, sai da kyar ya sha.

Sai dai shugaban karamar hukumar ya musanta wannan zargin. Inji Arewa Update.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp