Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa a ƙirji da ’yan daba suka yi a kofar gidan tsohon shugaban karamar hukumar Dala, Ibrahim Dan Isle, da ke Bachirawa, titin Sakatariya, layin Dan Isle.
Arewa Update ta rawaito cewa, Dan uwan marigayin, Abubakar Mahmud, ya shaida wa Arewa Updates cewa Ibrahim mabiyin tsohon shugaban karamar hukumar ne a siyasa, daga baya suka ɓaɓe, sai a baya-bayan nan suka shirya.
Ya ce Dan Islen ne ya gayyace shi gida domin karɓar naman Sallah, kuma da ya je ƙofar gidan ya kira shi a waya ya sanar da shi yana dakon fitowarsa, sai wasu ’yan daba suka afka masa inda suka soke shi a ƙirji abin da ya yi ajalinsa.
Ya ƙara da cewa sun je ofishin ’yan sanda na Bachirawa inda suka taho ƙafa da ƙafa da DPO domin bincike, amma abin bai yiwu ba, domin Dan Isle ya kwashe iyalinsa ya gudu daga unguwar, ya rufe gidansa, a cewar Abubakar.
’Yan uwan marigayin sun nemi hukumomi su yi bincike na adalci a kan lamarin.
Dangane da wannan alʼamari dai Arewa Updates ta yi ta kiran wayar Dan Isle amma wayarsa na nuna ʼbusyʼ, sai dai mun aika masa da saƙon kar-ta-kwana amma shiru babu amsa.
To amma muna ci gaba da jira, in ya magantu za mu sanar muku.
Ko a watan Mayun da ya wuce dai, Kansilan Mazabar Gobirawa a Dala, Hon. Ibrahim Danwaire, ya zargi Shugaban Karamar Hukumar Dala, Hon. Surajo Ibrahim Imam, da shirya masa wata kitimurmura inda aka lakada masa dukan tsiya a sakatariyar karamar hukumar, sai da kyar ya sha.
Sai dai shugaban karamar hukumar ya musanta wannan zargin. Inji Arewa Update.