fidelitybank

Ƴan fashin daji sun kai hari Zariya sun kuma kashe mutum 4

Date:

 

Yan fashin daji sun kai hari kan unguwar Kofar Kona a Zariya ta Jihar Kaduna, inda su ka kashe mutum 4 su ka kuma  ji wa da dama rauni.
Majiyoyi sun baiyanawa jaridar DAILY NIGERIAN cewa ƴan ta’addan sun shiga unguwar a ranar Litinin da misalin ƙarfe 10 na dare, in da su ka riƙa harbi kan me-uwa-da-wabi.
An ce bayan harbe-harben, yan bindigar sun kaɗa wani garken shanu cikin jeji.
Jaridar ta ce wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce mazauna unguwar sun yi ta kiran lambar ƴan sanda amma ba a amsa kiran nasu ba.
“mun yi ta kiran lambobin kar-ta-kwana na ƴan sanda amma ba amsa. Sai bayan ma yan bindigar sun ci karensu ba babbaka sannan yan sandan su ka zo.
“Wajen mutum 24 a ka garzaya da su asibitin Gambo Sawaba can a Ƙofar Gayan, in da 4 su ka rasu sakamakon harbin da a ka yi musu da yawa a jikunan su.
“Sun kuma tafi da garken shanu na wasu Fulani sabbin zuwa a yankin,” in ji shi.
Jaridar ta ƙara da cewa Kakakin Rundunar Ƴan Sanda ta Kaduna, Mohammed Jalige bai daga wayar da ta yi masa ba har zuwa lokacin da ta wallafa labarin.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp