Wasu ‘yan fashi da makami a safiyar Lahadi sun kai hari gidan yada labarai na Yinka Ayefele, Fresh FM da ke Ibadan, jihar Oyo tare da sace wasu abubuwa masu muhimmanci na ma’aikatan.
A cewar daya daga cikin ma’aikatan, b Abolade Salami a yayin shirin sa, ‘Agbo Oselu’ ya bayyana cewa, ‘yan fashin sun zo ne da misalin karfe 6 na safe dauke da bindigogi, kuma suka yi awon gaba da kayan ma’aikatan da ke bakin aiki.
Sunday Independent ta tattaro cewa, sassan abubuwan da aka sace sun hada da kudi da wayoyi da wasu abubuwa masu daraja da ba a ambata ba.