fidelitybank

Ƴan Boko Haram sun kashe manoma huɗu a Borno

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan ta’addar Boko Haram/ISWAP ne, sun kashe manoma akalla hudu a yankin Kerawa da ke kan iyaka a karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno.

An ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis tsakanin karfe 12 zuwa 1 na rana a yayin da manoman ke aikin gonakinsu.

Wannan na zuwa ne kawai watanni biyu bayan da wasu bama-bamai suka hallaka sama da mutane 30 a garin Gwoza.

Mai ba da shawara na gundumar Jimini, Bukar Aji da shugaban kungiyar al’ummar Kerawa Yakubu Ali, sun tabbatar da faruwar lamarin.

Jaridar DAILY POST ta bayar da rahoton cewa, garin Kerawa na kan iyaka da kasar Kamaru a tsaunin Mandara, inda aka san ‘yan ta’addan na buya.

A halin da ake ciki, jami’in ‘yan sanda na shiyya ta Gwoza ya ce bai san da faruwar lamarin ba, inda ya yi alkawarin tabbatar da rahoton.

DPO ya ce harin na iya kasancewa daga Kerawa ne na kasar Kamaru, ba wai Kerawa na Najeriya ba, ya kara da cewa an yi irin wannan kisan a wasu makonni baya a garin Kerawa na kasar Kamaru, amma jama’a sun rikitar da yankin Kerawa na Najeriya.

DAILY POST ta tuna cewa an taba ayyana Gwoza a matsayin halifancin ‘yan ta’adda a lokacin da aka kama ta a shekarar 2014, kafin daga bisani dakarun sojojin Najeriya su kwato su.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp