fidelitybank

Ƴan Boko Haram sun kashe Ɗalibai uku a jihar Yobe

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne sun kai hari a makarantar Faudiya Islamiyya da ke karamar hukumar Geidam a jihar Yobe da sanyin safiyar Juma’a, inda suka kashe dalibai uku, a cewar rundunar ‘yan sandan jihar Yobe.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Dungus Abdulkarim ya tabbatar da faruwar harin da misalin karfe 3:45 na safe.

A cewar sanarwar, maharan wadanda suka isa kan babura dauke da muggan makamai, sun mamaye makarantar ne da niyyar sace daliban.

Duk da haka, sun yanke shawarar kashe daliban nan da nan don guje wa “nauyin” kai su cikin daji.

Wani dalibi da ya yi yunkurin tserewa ya samu raunuka kuma an kai shi asibiti domin yi masa magani.

“An tabbatar; hedkwatar ‘yan sanda reshen Geidam ta samu rahoton da safiyar yau ta bakin wani mutum cewa an kai hari a wata makaranta.

“Mun tattara mutanenmu, kuma suka je can suka kwashe gawawwakin mutane uku da daya mai raunin harsashi wanda aka kwantar da shi a asibiti,” Abdulkarim ya shaida wa manema labarai.

Ya ci gaba da bayanin cewa, “Maharani sun zo ne a kan babura, kimanin 10 daga cikinsu, dauke da muggan makamai irin su AK-47 da sauran kayayyaki.

“Sun shiga makarantar ne suka dauki hudu daga cikin daliban, inda nan take suka kashe uku sannan suka raunata mutum daya.”

A cewar Abdulkarim, daya daga cikin daliban da suka samu raunuka ya bayyana cewa maharan sun shaida musu cewa sun yi niyyar sace su amma sun yanke shawarar kashe su a maimakon haka don gujewa matsalar safarar su.

Ya bayyana cewa a halin yanzu ‘yan sanda na gudanar da bincike don gano wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da gano musabbabin harin.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp