Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram da ISWAP ne sun kara kai hari kauyen Kautikari da ke karkashin karamar hukumar Chibok a jihar Borno, inda suka halaka ɗan dagacin kauyen, Bulama Wadir da wasu ƴan gudun hijira biyu da ke garin.
A cewar Vanguard, babu nisa sosai tsakanin kauyen Kautikari da garin Chibok, kuma harin ya auku ne bayan wani kazamin farmaki da suka kai a watan Janairun 2022, wanda suka yi garkuwa da fiye da mutane 10 yawanci mata da yara.
Haka zalika, sun banka wuta a wata majami’a mafi girma da ke makwabtaka da dajin Sambisa.
Farmakin ya na kara yawaita a kauyen Kautikari, Pemi, Korohuma da sauran kauyukua da ke zagaye da Chibok tun bayan watan Janairun wannan shekarar.