Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da matar da diyar Kwamishinan Muhalli na Jihar Filato, Idi Bamaiyi.
Majiyoyin iyalan sun shaida wa gidan talabijin na Channels cewa, an yi garkuwa da uwa da ‘yarta a safiyar ranar Asabar lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki gidan kwamishinan.
Sai dai sun tabbatar da cewa, an kai rahoton faruwar lamarin ga jami’an tsaro a kokarinsu na ganin an dawo da wadanda abin ya shafa.
An ce maharan sun shiga gidan ne da sanyin safiya kafin su yi awon gaba da mutanen a garin Gindiri da ke karamar hukumar Mangu ta jihar.
A cewar shaidun gani da ido, harin ya dauki kimanin sa’a guda ne yayin da ‘yan bindigar suka tare wasu manyan tituna a cikin garin yayin da ake ci gaba da kai farmakin.
Garin na Gindiri da kewaye dai na fuskantar hare-hare daga wasu ‘yan bindiga a cikin ‘yan makonnin da suka gabata inda aka yi awon gaba da wasu mazauna garin.