fidelitybank

Ƴan bindiga sun yi awon gaba da mata da ƴar Kwamishina

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da matar da diyar Kwamishinan Muhalli na Jihar Filato, Idi Bamaiyi.

Majiyoyin iyalan sun shaida wa gidan talabijin na Channels cewa, an yi garkuwa da uwa da ‘yarta a safiyar ranar Asabar lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki gidan kwamishinan.

Sai dai sun tabbatar da cewa, an kai rahoton faruwar lamarin ga jami’an tsaro a kokarinsu na ganin an dawo da wadanda abin ya shafa.

An ce maharan sun shiga gidan ne da sanyin safiya kafin su yi awon gaba da mutanen a garin Gindiri da ke karamar hukumar Mangu ta jihar.

A cewar shaidun gani da ido, harin ya dauki kimanin sa’a guda ne yayin da ‘yan bindigar suka tare wasu manyan tituna a cikin garin yayin da ake ci gaba da kai farmakin.

Garin na Gindiri da kewaye dai na fuskantar hare-hare daga wasu ‘yan bindiga a cikin ‘yan makonnin da suka gabata inda aka yi awon gaba da wasu mazauna garin.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp